A jawabinsa yayin taron jakadan kasar Rwanda a kasar Sin, Charles Kayonga ya bayyana cewa, taron yau zai taimaka wajen hada kan kasashen Afirka da kamfanonin kasar Sin, da kyautata yanayin zuba jari na kasashen Afirka, da taimakawa kamfanonin kasar Sin su je Afirka su zuba jari.
A nasa bangare, shugaban cibiyar musanyar al'adu da harkokin diflomasiyya ta kasar Sin, Ma Zhenxuan, ya ce yana fatan taron na yau zai kara fahimtar juna tsakanin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka, da karfafa zumunci tsakanin al'ummominsu.(Murtala Zhang)