in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi Allah wadai da harin da aka kai Burkina Faso
2018-03-03 14:03:15 cri
Tarayyar Afrika AU ta yi Allah wadai da murya kakkausa, kan hare- haren da aka kai Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso a jiya Juma'a.

Rundunar 'yan sanda Burkina Faso ta tabbatar da aukuwar harin da rahotanni suka ce an kai wa ofishin jakadancin Faransa dake Ouagadougou da kuma hedkwatar rundunar sojin kasar.

Mutane sama da 10 ne suka mutu, ciki har da mahara biyu da wasu jami'an tsaro.

Wata sanarwar da AU ta fitar, ta ce shugaban hukumar kula da ayyukanta Moussa Faki Mahamat, ya ce tarayyar ta na tare da al'umma da gwamnatin Burkina Faso a wannan mayuwacin lokaci.

A nasa bangaren, cikin wata nsanarwa da ya fitar, ministan harkokin wajen Faransa Jean Yves Le Drian, ya tabbatar da harin da aka kai ofishin jakadancin kasarsa dake birnin Ouagadougou.

Ministan ya ce jami'an tsaron kasar da taimakon jami'an tsaron ofishin jakadancin, sun tunkari maharan inda suka rage ta'adin harin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China