in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso ta katse huldar diflimasoya da yankin Taiwan
2018-05-24 21:20:31 cri
Ministan harkokin wajen Burkina-Faso Alpha Barry ya bayyana a yau Alhamis cewa, kasarsa ta katse huldar diflomasiya da yankin Taiwan na kasar Sin. Game da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka shirya a wannan rana cewa, kasar Sin ta nuna yabo kan wannan sanarwar.

Wata sanarwa da ma'aikatar ta rabawa manema labarai ta ce, gwamnatin Burkina-Fason ta dauki wannan mataki ne a yau. Shugaban kasar Faso Marc Christian Kabore ya umarci ma'aikatar harkokin wajen da hadin gwiwa ta kasar, da ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka wajaba na rufe ofishin jakadancin kasar dake Taipei da ma na Taiwan dake kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China