in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Oman sun sanar da kulla muhimmiyar dangantaka
2018-05-25 15:35:59 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sarkin Oman Sultan Qaboos Bin Said, sun taya juna murnar kafuwar muhimmiyar dangataka tsakanin kasashen su. Shugabannin biyu sun aikewa juna sakon murnar cimma wannan mataki ne a jumma'ar nan, a gabar da kasashen biyu ke jinjinawa juna game da yadda suka shafe shekaru 40, tun bayan kulla huldar diflomasiyya.

A cikin sakon sa, shugaba Xi ya ce alakar kasar sa da Oman ta kai ga matsayin koli, inda ta shafi manya, kuma muhimman fannoni, karkashin inuwar shawarar nan ta ziri daya da hanya daya, matakin da ya haifarwa al'ummun su alfanu mai tarin yawa.

Shugaban na Sin ya kara da cewa, yana martaba alakar sassan biyu, yana kuma da burin daga matsayin ta, ta yadda za ta kai ga dama mai daraja da za ta amfani kasashen bisa hadin gwiwar sarkin na Oman. Ya ce wannan gaba ta cikar dangantakar kasashen biyu shekaru 40, wata dama ce ta cimma wannan nasara.

A nasa bangare kuwa, Sarki Qaboos cewa yayi, Oman a shirye take ta karfafa muhimmiyar alakar dake tsakanin ta da Sin, ta yadda hakan zai haifar da alfanu, da kuma biyan bukatun al'ummun kasashen biyu.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China