in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in Koriya ta arewa: Kasar na sake duba ko za ta halarci ganawa tsakanin shugabanninta da na Amurka ko a'a
2018-05-17 11:04:56 cri
Mataimakin ministan harkokin waje na farko na Koriya ta arewa Kim Kye-gwan ya bayyana a cikin wata sanarwa a jiya cewa, idan har gwamantin Donald Trump na Amurka tana son ta tilasta Koriya ta arewa ta yi watsi da shirinta na raya makaman nukiliya a nata bangare kawai. To, Koriya ta arewan za ta sake duba ko za ta halarci ganawar da ake shirin gudanar tsakanin shugabannin Koriya ta Arewa da na Amurka.

A cewar Kim Kye-gwan, kafin ganawar shugabannin kasashen biyu, bai dace kasar Amurka ta fadi wasu kalaman ta da hankali ga daya bangaren da zai halarci ganawar ba. Matsayin da mai ba da taimako ga shugaban Amurka kan harkokin tsaron kasar John Bolton ya gabatar kwanan baya, inda ya ba da misali da "matakin kawar da nukiliya na Libya" bisa manufa "Yin watsi da nukiliya kana a ba da tallafi ", ba wata hanya ce dake bayyana burin daidaita lamarin bisa shawarwari ba. Ya ce, muddin ana son a kawar da makaman nukiliya a zirin koriya, wajibi ne a Amurka ta daina yiwa manufofin Koriya ta Arewa karan tsaye, da ma daina yi mata barazana. (Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China