in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka za ta soke takunkumi kan Koriya ta Arewa idan ta kawar da makaman nukiliya
2018-05-14 14:00:10 cri
Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya bayyana a ranar 13 ga wata cewa, idan Koriya ta Arewa ta kawar da makaman nukiliya daga duk fannoni, kasar Amurka za ta soke takunkumin da aka kakabawa kasar a fannin tattalin arziki, da amincewa kamfanonin Amurka masu zaman kansu su zuba jari gare ta.

Mr Pompeo ya bayyana a wannan rana cewa, idan Koriya ta Arewa ta yi watsi da makaman nukiliyarta, kasar Amurka za ta soke takunkumi da aka kakabawa kasar Koriya ta Arewa tare da taimake ta wajen samun wadata.

Pompeo ya yi nuni da cewa, kasar Amurka za ta taimakawa kasar Koriya ta Arewa a fannonin makamashi, wutar lantarki, kayayyakin more rayuwar yau da kullum, aikin gona da sauransu. Kana ya jaddada cewa, sharadin da aka saka kan wannan batu shi ne kawar da makaman nukiliya a dukkan fannoni a zirin Koriya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China