in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron ministocin tsaron kasa na kungiyar SCO
2018-04-25 13:03:00 cri
An gudanar da taron ministocin tsaron kasa na kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai wato SCO karo na 15 a jiya 24 ga wata a nan birnin Beijing, inda memban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan tsaron kasar Wei Fenghe ya shugabanci taron, tare da yin wani jawabi.

Shugabannin hukumomin tsaron kasa da na sojoji na kasashe membobin kungiyar SCO wato Rasha, Indiya, Kazakhstan, Kyrgyz, Pakistan, Tajikistan da kuma Uzbekistan, da kuma wakilan sashen sakatariyar kungiyar SCO, da kwamitin gudanarwa na yaki da ta'addanci a yankuna sun halarci taron.

A cikin jawabinsa, Wei Fenghe ya bayyana cewa, taken taron a wannan karo shi ne "kafa kungiya mai buri iri daya, da yin kirkire-kirkire, da hadin gwiwa don neman bunkasuwa tare". Ya ce kamata a aiwatar da ayyukan da shugabannin kasa da kasa suka cimma daidaito a kan su, da inganta hadin gwiwarsu a fannin kiyaye tsaron kasa.

Wei Fenghe ya yi nuni da cewa, ya kamata a ci gaba da bin tunanin Shanghai, da kara yin hadin gwiwa a fannonin mu'amalar dake tsakanin manyan shugabanni, da atisayen soja, aikin soja, horaswa da sauransu, musamman ma batun hadin kan wajen yaki da ta'addanci, don tabbatar da zaman lafiya a yankuna har ma a dukkan duniya gaba daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China