in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan majalisar dokokin Sin ya kai ziyara kasar Namibia
2018-05-18 21:23:58 cri
Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'a ta kasar Sin Li Zhanshu ya kai ziyarar sada zumunci a hukumance kasar Namibia daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Mayu, bisa gayyatar kakakin majalisar dokokin kasar ta Namibia Peter Katjavivi, inda ya yi kira da a karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

A lokacin da yake Windhoek, babban birnin kasar, Li ya gana da shugaban kasar Hage Geingob da tsohon shugaban kasar Sam Nujoma. Haka kuma Li ya tattauna da Katjavivi da shugabar majalisar zartarwar kasar Magreth Mensah-Williams.

Mr Li ya ce ziyarar da Geingob ya kawo wa kasar Sin a watan Maris din da ya gabata ya bude wani sabon babi a dangatakar dake tsakanin kasashen Sin da Namibia, abin da ya sa shugabannin kasashen biyu yanke shawarar daga matsayin alakar kasashen zuwa manyan tsare-tsare.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin tana fatan sassan biyu za su hada kai wajen karfafa tattaunawa bisa manufa da daidaita shiryen-shiryen ci gaba ta yadda zai dace da shawarar ziri daya da hanya daya, da dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka(FOCAC), da bunkasa hadin gwiwa a fannin gina ababan more rayuwa da raya masana'antu ta yadda za su amfanawa al'ummon kasashen biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China