in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in kasar Sin ya kai ziyara kasar Habasha
2018-05-12 15:44:01 cri

Bisa gayyatar da shugabar majalisar wakilan jama'ar kasar Habasha Muferiat Kamil da shugabar majalisar dokokin kasar Keria Ibrahim suka yi masa, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Li Zhanshu ya kai ziyara kasar Habasha tun daga ranar 9 zuwa 12 ga wannan wata, inda ya gana da shugaban kasar Habasha Mulatu Teshome da firaministan kasar Abiy Ahmed, har ma ya yi shawarwari tare da Muferiat Kamil da Keria Ibrahim.

Yayin da yake ganawa da shugaba Teshome, Li Zhanshu ya isar masa da gaisuwa daga shugaban kasar Sin Xi Jinping. Ya ce, wannan ne karo na farko da ya kai ziyara kasar waje tun bayan da ya zama shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, wannan ya shaida cewa Sin ta dora muhimmanci ga raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Habasha da kuma nahiyar Afirka. Sin tana son hada kai tare da kasar Habasha wajen inganta hadin gwiwa da sada zumunta a tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi.

A nasa bangare, shugaba Teshome ya nuna godiya ga kasar Sin bisa ga goyon bayan da ta dade tana nunawa kasar Habasha. A yayin da ake raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, kasar Habasha tana son hada kai tare da kasar Sin wajen inganta dangantakar abokantaka ta hadin gwiwarsu bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China