in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban zaunannen kwamitin NPC ya ziyarci Mozambique
2018-05-16 11:14:46 cri

Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC Li Zhanshu ya kai ziyarar karfafa dangantaka a kasar Mozambique tsakanin ranakun Asabar zuwa Talata, da nufin kyautata mu'amala tsakanin kasashen biyu.

Li, ya gana da shugaban kasar Mozambique Filipe Nyusi a Maputo, babban birnin kasar, kana ya zanta da shugabar majalisar dokokin kasar Veronica Macamo.

A lokacin ganawar tasu da shugaba Nyusi, Li ya ce, kasar Sin ta taimakawa kasar Mozambique a kokarinta na neman 'yancin kai da kuma samun dawwamammen ci gaba, kuma za ta ci gaba da taimakawa Mozambique din wajen samun ci gaba cikin sauri.

A nasa bangaren, shugaba Nyusi ya ce, kasar Mozambique a shirye take ta shiga shirin raya shawarar ziri daya da hanya daya, da kuma zurfafa mu'amala da kasar Sin a fannonin aikin gona, makamashi, masana'antu, yawon bude ido da gina kayayyakin more rayuwa, da nufin daga martabar dangantakar dake tsakanin kasashe biyu zuwa matsayin koli.

A lokacin tattaunawarsa da shugabar majalisar dokokin kasar Macamo, Li ya ce, NPC a shirye take ta kulla kyakkyawar alakar abokantaka da majalisar dokokin kasar, da kuma yin musayar kwarewa a matakai daban daban da takwararta ta kasar Mozambique, da kuma tabbatar da ganin an aiwatar da dukkan yarjejeniyoyin hadin gwiwar da aka kulla tsakanin bangarorin biyu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China