in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an wanzar da zaman lafiya na kasar Sin 190 sun tafi Mali
2018-05-17 10:28:39 cri
Jimilar jami'an wanzar da zaman lafiya 190 ne suka bar Jinan, babban birnin lardin Shandong na kasar Sin a jiya Laraba, domin tafiya kasar Mali dake yammacin Afrika, da nufin gudanar da aiki na tsawon shekara guda karkashin shirin wanzar da zaman lafiya na MDD.

Jami'an na daga cikin ayari mai mambobi 395, wanda ya kasance ayari na 6 da aka tura kasar.

Ayarin, zai gudanar da ayyukan da suka hada da samar da tsaro da kula da wadanda suka ji rauni.

Za kuma a dora musu aikin kula da tituna da hanyoyin jirgi da kuma tsaftar muhalli da kare barkewar cututtuka.

Tun daga farkon bana ne aka fara ba jami'an horo kan dabarun yaki.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China