in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi Allah wadai da harin da ya hallaka ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a Mali
2018-03-01 18:41:12 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da harin da aka kai yankin Mopti na kasar Mali, harin da ya halaka 'yan kasar Bangadesh 4 dake aikin wanzar da zaman lafiya, lokacin da wani abun fashewa ya tarwatse kana wasu mutane 4 kuma suka jikkata.

Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan da wasu sojojin kasar Mali 6 suka mutu a wani harin da aka kaddamar a tsakiyar kasar.

Wata sanarwar da kakakin Guterres Stephane Dujarric ya fitar, ta ruwaito shi ne yana cewa, hare-haren da aka kaiwa jami'an MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya tamkar aikata laifukan yaki ne karkashin dokokin kasa da kasa, don haka wajibi ne a zakulo tare da hukunta wadanda suka aikata shi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China