Kwamitin sulhu na MDD ya ba da wata sanarwa a jiya Lahadi 15 ga wata, inda ya yi Allah wadai da kakkausar murya da harin da 'yan ta'adda suka kaiwa MINUSMA, rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya ta MDD dake Timbuktu na kasar Mali.
Rahotanni sun ce, harin ya haddasa mutuwar sojan kiyaye zaman lafiya 'dan asalin Burkina Faso, yayin da wasu sojoji da dama suka ji rauni. (Amina Xu)