'Yan wasan sun hada da Junior Lokosa da Simeon Nwanko, da Leon Balogun, da Wilfred Ndidi, da Etebo Oghenekaro, da Jeol Obi da Trone Ebuehi.
Yanzu haka dai an shirya 'yan wasan za su yi wasan sada zumunta da Jamhuriyar demokiradiyar Congo a ranar 28 ga watan Mayu da muke ciki, kafin su isa London inda za su fafata da Three Lions a filin wasa na Wembley a ranar 2 ga watan Yuni kafin daga bisani su fafata da Jamhuriyar Czech a ranar 6 ga watan Yuni.
Najeriya dai na rukuni na 4 hudu a gasar cin kofin duniya da za a yi a kasar Rasha, tare da kasashen Argentina da Iceland da kuma Croatia. (Ibrahim)