in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da gasar harshen Sinanci a Kenya
2018-05-12 15:49:52 cri
A jiya ne aka shiryawa daliban kwaleji 'yan kasashen waje wata gasar harshen Sinanci mai suna " Chinese Bridge" karo na 17 a birnin Nairobin kasar Kenya.

Ofishin jakadancin kasar Sin dake Kenya tare da hadin gwiwar cibiyar Confucius dake jami'ar Nairobi da kungiyar tattalin arziki da cinikayya ta Kenya da Sin(KCETA) ne suka shirya gasar, wadda ta hallara matasa 16 wadanda suka nuna kwarewarsu ta magana da harshen Sinanci.

A jawabinsa jami'in ofishin jakadancin Sin dake Kenya Li Xuhang, ya yabawa matasan da suka shiga wannan gasa, yana mai cewa harshe muhimman bangare ne wajen bunkasa musayar al'adu.

Li ya yi imanin cewa, ta hanyar wannan gasa, matasan za su kara fahimtar harshe da al'adun Sinawa.

Ya kuma bayyana cewa, yadda ake koyar da Sinanci da al'adun Sinawa ya bunkasa kwarai a kasar Kenya. Ya kuma mika godiya ga yadda aka bude cibiyoyin Confucius har guda hudu a manyan jami'o'in kasar.

An gabatar da jawabai da kade-kade da raye-raye da tsoffin wake-wake da sauran fasahohi yayin gasar da aka gudanar a tsohuwar jami'ar Kenya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China