in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya ta harba tauraron dan-Adam mai kula da tsarin muhalli na farko
2018-05-12 15:25:28 cri
A jiya ne kasar Kenya ta harba tauraron dan-Adam na nano na farko zuwa sararain samaniya, a kokarin da gwamnatin kasar ke yi na bunkasa binciken sararin samaniya don magance matsalar abinci, muhalli da kuma lafiya.

Jami'ar Nairobi da ofishin MDD mai kula da harkokin zirga-zirgar sararin samaniya(UNOOSA) da hukumar binciken sararin samaniya ta kasar Japan(JAXA) ne suka kera dan karamin tauraron dan-Adam din mai fadi da tsayi mita goma-goma.

Babban sakatare a ma'aikatar harkokin waje da cinikayyar kasa da kasa ta kasar Kenya Macharia Kamau ya yaba da yadda aka harba tauraron dan-Adan din cikin sararin samaniya, yana mai cewa zai sanya kasar Kenya kasancewa, cibiyar binciken sararin samaniya ta shiyyar.

Kamau ya ce wannan rana ce mai muhimmanci a tarihin binciken sararin samaniya na kasar Kenya, kuma zai taimakawa kasar wajen magance kalubalen da suka shafi matsalar canjin yanayi kamar fari, ambaiyar ruwa da yadda ake hasarar muhallin halittu.

Ya kara da cewa, harba tauraron dan-Adam din zuwa sararin samaniya, zai taimaka a fannin hasashen yanayi da inganta matakan tunkarar bala'u a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China