Kakakin rundunar tsaron kasar Isra'ila Jonathan Conricus ya bayyana a wannan rana cewa, da daren ranar 9 ga wata, da kuma safiyar 10 ga wata, rundunar soja ta Iran ta "Quds Force", ta harba rokoki kimanin 20 daga sansaninta dake kasar Sham, zuwa ga tuddan Golan dake karkashin ikon Isra'ila, daga bisani kuma sojojin Isra'ila suka kaddamar da hari kan na'urorin da Iran ta jibge a kasar Sham. (Amina)