in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta kakabawa sassan Iran takunkumi
2018-05-11 10:53:43 cri
Sashen baitulmalin Amurka ya bayyana kakabawa wasu 'yan kasar Iran da wasu kamfanoni ta 9 takunkumi, a wani mataki na dakile musayar kudade mai tasirin gaske, da kasar ta Iran ke yi tsakanin ta da hadaddiyar daular Larabawa.

Wannan mataki dai na zuwa ne, yayin da shugaban Amurka Donald Trump, ya ayyana janyewar kasar sa daga yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran.

Wata sanarwa da baitulmalin Amurkan ya fitar, ta ce Amurka da hadaddiyar daular Larabawa, sun amince su yi hadin gwiwa, wajen dakile tasirin musayar kudi da Iran, wanda kafin hakan ke samarwa dakarun rundunar juyin juya halin Iran din ko IRGC-QF miliyoyin dalolin Amurka, kudaden da dakarun ke amfani da su, wajen aiwatar da harkokin su na tallafawa kungiyoyin yankin dake mara masu baya.

Sakataren baitulmalin Amurka Steven Mnuchin, ya jaddada cewa, gwamnatin Iran da babban bankin kasar, na amfani da damar samun musayar kudade ta hadaddiyar daular Larabawa, wajen tallafawa rundunar IRGC-QF. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China