in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birnin Beijing zai dauki matakin kau da sauro
2018-05-11 18:56:50 cri
Birnin Beijing na kasar Sin na shirin daukar mataki na kau da sauro a tsakiyar watan Mayu da muke ciki, da magance yaduwar wasu cututtuka irinsa zazzabin dengi, kamar yadda hukumar lafiyar birnin ta sanar.

Manufar wannan matakin ita ce kau da ruwa dake cikin wasu ramuka, musamman ma a dakunan dake karkashin kasa, da lambatu, da wuraren shakatawa, da wuraren da ake gudanar da aikin gine-gine, da cibiyoyin kula da shara, da makamantansu, kamar yadda Liu Zejun, jami'in hukumar kula da lafiya da kayyade iyali na gwamnatin birnin Beijing ya bayyana.

Sauran matakan da za a dauka a wannan karo sun hada da sanya kifaye masu cin sauro a cikin tabkuna, da fesa maganin sauro a wasu wuraren dake da wahalar kawar da ruwa, misali lambatu dake karkashin kasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China