in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ganawar dake tsakanin shugabannin Sin da Koriya ta Arewa ta taimakawa raya dangantakar dake tsakaninsu yadda ya kamata
2018-05-09 20:57:25 cri
Shugaban kwamitin koli na JKS kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya zanta da shugaban kasar Koriya ta arewa, kuma shugaban jam'iyyar WPK Kim Jong Un a birnin Dalian na lardin Liaoning dake arewa maso gabashin kasar Sin, tsakanin ranekun 7 da 8 ga watan nan na Mayu. Game da wannan batu, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a yau 9 ga wata cewa, yanzu haka an shiga muhimmin lokacin samun canji a zirin Koriya, shugabannin kasashen Sin da Koriya ta Arewa sun yi mu'amala bisa manyan tsare-tsare, wanda ya sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, da taimakawa wajen cimma burin kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, da samun zaman lafiya mai dorewa a zirin. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China