in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan Birtaniya da Rasha za su daidaita rikici ta hanyar tattaunawa
2018-03-15 19:53:50 cri
Dangane da rikicin diplomasiyya a tsakanin kasashen Birtaniya da Rasha, yau Alhamis Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, kasar Sin na fatan sassa daban daban masu ruwa da tsaki za su bi diddigin batu su kuma bankado gaskiyar lamarin, kana su daidaita rikicin ta hanyar tattaunawa yadda ya kamata.

A 'yan kwanakin nan, rikicin diplomasiyya a tsakanin Birtaniya da Rasha sakamakon yunkurin hallaka tsohon dan leken asirin kasar Rasha mai cin tudu biyu Sergei Skripal a Birtaniya yana ci gaba da daukar wani salo. A yammancin jiya ne, kwamitin sulhu na MDD ya kira taron gaggawa domin nazartar lamarin. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China