in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen Rasha da Iran za su gana game da yarjejeniyar nukiliyar Iran
2018-04-27 10:55:57 cri
Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov, zai gana a gobe Asabar, da takwaransa na Iran Mohammed Javad Zarif, game da yarjejeniyar Nukiliyar Iran, bayan Amurka da Faransa sun yi barazanar rushe ta.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Rasha, Maria Zakharova ce ta bayyana haka a jiya Alhamis, yayin wani taron manema labarai, inda ta ce manyan jami'an biyu za su gana ne a gefen taron ministocin wajen Rasha da Iran da Turkiyya game da Syria da zai gudana gobe a Moscow.

A cewarta, yayin tattaunawar, za a yi musayar ra'ayi game da batutuwan da suka shafi kasa da kasa da yankuna, ciki har da yadda batun aiwatar da kunshin yarjejeniyar nukiliyar Iran ke kara shiga mummunan yanayi.

Maria Zakharova, ta ce Rasha ta damu ainun da jawaban da shugaban Amurka Donald Trump da takwaransa na Faransa Emmanuel Macron su ka yi a baya-bayan nan game da yarjejeniyar nukiliyar Iran.

Ta ce yarjejeniyar ta cimma daidaito wadda ta kiyaye dukkan muradun wadanda suka amince da ita. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China