in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani sabon hari da aka kai wata mujami'a a Nijeriya ya yi sanadin rayuka a kalla 7
2018-04-27 10:07:06 cri
A kalla masu ibada 7 ne suka mutu yayin wani sabon harin da wasu 'yan bindiga da ba a san ko su waye ba, suka kai wata mujami'a da sanyin safiyar jiya Alhamis a Jihar Benue dake arewa maso tsakiyar Nijeriya.

Shugaban karamar hukumar Logo ta jihar, Richard Nyajo, ya ce wasu mutane sun farwa wata mujami'a da makarantar firamare a yankin, inda suka yi ta harbe-harbe.

A cewarsa, galibin wadanda harin ya rutsa da su na neman mafaka ne a mujami'ar da makarantar dake unguwar Mbamono, saboda harin da aka kai kafin na safiyar jiyan, ya raba su da matsugunansu, yana mai cewa mafi yawa daga cikinsu suna barci a lokacin da aka kai harin.

Har yanzu babu takamaiman adadin wadanda suka jikkata. Sai dai ya ce ana zargin makiyaya da kai harin.

Jihar Benue ta kasance a yankin tsakiyar Nijeriya, inda ta raba tsakanin yankunan arewaci da kudancin kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China