in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya zai sake tsayawa takara
2018-04-09 20:15:26 cri
Manyan kusoshin jam'iyya mai mulki a tarayyar Najeriya, da ma wasu jami'an gwamnatin kasar, sun tabbatar da cewa shugaban kasar mai ci Muhammadu Buhari, zai sake tsayawa takarar shugabancin kasar, a babban zaben kasar na badi.

Kafofin watsa labaran kasar sun rawaito gwamnan jihar Kaduna Nasir El Rufa'i na cewa, shugaban kasar ya shaidawa wani taron shugabannin jam'iyyarsa ta APC wannan aniya tasa.

A wata zantawa da ya yi ta wayar tarho da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, kakakin shugaban kasar Garba shehu, ya tabbatar da wannan batu, yana mai cewa ko shakka babu shugaban Najeriyar ya bayyanawa 'yan jam'iyyar tasa, burin sa na tsayawa takara a babban zaben kasar dake tafe cikin farkon shekara mai zuwa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China