Rahoton hakkin dan Adam na Amurka ya sake zargin yanayin hakkin dan Adam na sauran kasashe
A kwanakin baya ne ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta fitar da rahoton kare hakkin dan Adam na kasa da kasa na shekarar 2017, inda ta sake yin bincike kan yanayin kare hakkin dan Adam na wasu kasashe. Manazarta siyasa na kasar Amurka suna ganin cewa, kasar Amurka tana son boye munanan yanayin kare hakkin dan Adam din ta, don ta zargi yanayin kare dan Adam na sauran kasashe.
Mataimakin forfesa na siyasar kasashen gabashin Asiya da dangantakar kasa da kasa na jami'ar Houston ta kasar Amurka Peter J. Li ya bayyana cewa, a shekarun baya baya nan, yanayin kare hakkin dan Adam na kasar Amurka ya tsananta, inda ake nuna bambanci ga jama'ar da suke da bambancin al'adu da ra'ayoyin siyasa, kasar Amurka ta kasance kasar da ta ke nuna bambanci ga juna a wannan fanni. (Zainab)