Xi Jinping ya ce, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin zai kawo ziyara kasar Sin a watan Yunin wannan shekara, inda kuma zai halarci taron kolin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai da za a yi a birnin Qingdao. Shugaba Xi yana sa ran ganawa da shugaba Putin domin raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma yin hadin gwiwa da sauran mambobin kungiyar domin neman ci gaban kungiyar a nan gaba.
A nasa bangare, Sergei Lavrov ya ce, Sin da Rasha suna mutunta dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD, kuma dukkansu suna son karfafa hadin gwiwarsu bisa tsarin hadin gwiwar kasa da kasa. (Maryam)