in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi zai kai ziyara kasar Rasha a matsayin manzon musamman na Shugaba Xi Jinping
2018-03-26 19:43:34 cri
Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi zai kai ziyara kasar Rasha, a matsayin manzon musamman na Shugaba Xi Jinping tun daga ranar 27 zuwa 28 ga wannan wata.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, wannan ziyara ta shaida matsayin musamman, game da dangantakar dake tsakanin Sin da Rasha. Hua ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau 26 ga wata cewa, Vladimir Putin ya sake zama shugaban kasar Rasha, ana kuma fuskantar sabuwar damar bunkasuwa a tsakanin Sin da Rasha, a wannan gaba ne Wang Yi zai gana da shugabannin kasar Rasha, kana zai yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergej Lavrov, inda za su yi musayar ra'ayoyi kan ganawar da ta wakana tsakanin manyan shugabannin kasashen biyu, da sa kaimi ga hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu a manyan fannoni da sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China