in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban bankin tsakiya na kasar Sin ya karfafawa hukumomi masu zaman kansu gwiwar zuba jari da kasuwanci a nahiyar Afirka
2018-04-21 16:59:05 cri
Shugaban bankin tsakiya na kasar Sin Yi Gang, ya halarci taron ministocin kudi da shugabannin bankunan tsakiya na kungiyar G20 a birnin Washington na kasar Amurka, daga ranar 19 zuwa 20 ga wannan watan.

Yayin taron, Yi Gang ya karfafawa hukumomi masu zaman kansu gwiwar su zuba jari da kasuwanci a nahiyar Afirka. La'akari da yadda aikin zuba jari a nahiyar Afirka ke daukar lokaci tare da fuskantar hadari, ya ba da shawarar yin amfani da tsari mai dorewa na hada-hadar kudi da zuba jari. Bankin jama'ar kasar Sin da bankin raya kasashen Afirka sun kafa asusun raya nahiyar Afirka tare, inda yawan kudinsa ya kai dala biliyan 2 a shekarar 2014, wanda kuma ya gudanar da aikinsa yadda ya kamata ya zuwa yanzu. Asusun raya Sin da Afirka da bankin raya kasa da kasa ya kafa, shi ma ya samar da goyon baya a fannin harkokin kudi ga kasashen Afirka. Wadannan asusu sun yi amfani da albarkatun yankin dake cikin asusun wajen tabbatar da zuba jari da tattara kudi mai dorewa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China