in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan Nijeriya sun yi tir da kutsen da aka yi wa majalisar dattawan kasar
2018-04-20 10:06:06 cri
'Yan Nijeriya sun yi tir da dauke sandar majalisar dattawa da wasu bata gari suka yi a ranar Laraba da ta gabata, inda suka ce batu ne da ya samo asali daga harkar siyasa.

Sandar alama ce ta girma ga zaurukan majalisun dattawa da na wakilan kasar.

Wadanda suka yi tsokaci kan al'amarin, sun bayyana shi a matsayin abun kunya ga Nijeriya, wadda ta fi kowacce kasa yawan al'umma a nahiyar Afrika.

'Yan sanda dai sun ce sun gano sandar da wasu da ba a san ko su waye ba suka sace daga zauren majalisar dattawa.

Ana zargin wasu bata gari da kutsawa zauren majalisar yayin da ta ke zamanta a ranar Laraba, inda suka yi awon gaba da sandar.

Mai Magana da yawun 'yan sanda a kasar Aremu Adeniran, ya ce an jefar da sandar ne a karkashin wata gadar sama, dake kusa da kofar shiga cikin birnin Abuja. Wani dake wucewa ne ya gani tare da shaidawa 'yan sandan.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kakakin majalisar Sabi Abdullahi, ya zargi 'dan majalsiar da aka dakatar Ovie Omo-Agege da jagorantar matasan da suka sace sandar yayin zaman majalisar.

Abdullahi Sabi ya bayyana al'amarin a matsayin babban laifin bijerewa kasa, wanda zai haifar da karbe ragamar majalisar dattawan.

A nasa bangaren, mataimakin shugaban majalsiar wakilan kasar Yusuf Lasun, ya bayyana dauke sanadar a matsayin abun da ya kunyata demokradiyyar kasar, yana mai cewa, zauren majalisar na 8 zai tabbatar da demokradiyya ta yi aiki a kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China