in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF: 'yan ta'adda sun sace a kalla yara 1,000 a Nijeriya, tun daga shekarar 2013 kawo yanzu
2018-04-14 12:14:27 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce a kalla yara 1,000 ne kungiyar Boko Haram ta sace a yankin arewa maso gabashin Nijeriya tun daga shekarar 2013, a lokacin da ake tsaka da ci gaba da kai hare-hare kan makarantu.

A cewar UNICEF, tun bayan da rikicin Boko Haram ya barke a arewa maso gabashin Nijeriya kusan shekaru 9 da suka gabata, a kalla malamai 2,295 aka kashe yayin da aka lalata makarantu sama da 1,400, inda ya ce har yanzu ba a bude galibin makarantun ba saboda yadda hare-haren suka lalata su ko kuma saboda rashin tsaro da har yanzu ake fama da shi.

Batun na sace yara ya kara jan hankalin al'umma ne a lokacin da aka sace 'yan mata 276 daga sakandaren garin Chibok a shekarar 2014.

Shekaru 4 ke nan tun bayan aukuwar al'amarin, amma har yanzu ba a kai ga dawo da sama da 100 daga cikinsu ga iyalansu ba.

Har ila yau, asusun ya ce harin baya-bayan nan da aka kai Sakandaren garin Dapchi, inda 'yan mata 5 suka rasa rayukansu alamu ne dake nuna cewa a wurare kalilan ne kawai yara ke da tabbacin tsaro a yankin arewa maso gabashin Nijeriya

Asunsun, ya lashi takobin goyon bayan hukumomin Nijeriya, wadanda suka jajirce wajen tabbatar da tsaro a makarantu ta hanyar ba su kariya daga rikice-rikice. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China