in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan kokari tare da kasa da kasa wajen hadin gwiwar bude kofa da samun moriyar juna
2018-04-17 19:47:53 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Talata a nan birnin Beijing cewa, hakikanin abun da ya haifar da matsalar cinikayya a tsakanin Sin da Amurka, shi ne rashin fahimta tsakanin masu ra'ayin cudanya da bangarori daban daban, da masu ra'ayin bangare daya, da kuma tsakanin cinikayyar duniya cikin 'yanci, da masu ra'ayin bada kariya ga cinikayya.

Ta ce bisa tarihin duniya, an shaida cewa, rufe kofa zai rufe hanyar hadin gwiwar dake tsakanin kasa da kasa, don haka ya kamata a bude kofa da inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashen duniya.

A kwanakin baya, yayin da ake shawarwari game da tattalin arziki a tsakanin Sin da Japan, da tsakanin Sin da Indiya, Japan da Indiya sun nuna goyon baya ga tsarin ciniki tsakanin bangarori daban daban bisa ka'idojin da aka tsara, suna masu cewa ya kamata a tabbatar da tsarin yin cinikayyar duniya cikin 'yanci karkashin jagorancin kungiyar WTO.

Shugabannin kasa da kasa da na kungiyoyin duniya daban daban, su ma sun nuna goyon bayan su ga wannan ra'ayi. A gun taron manema labarun da aka gudanar a ranar 17 ga wata, Hua Chunying ta bayyana hakan, yayin da ta amsa tambaya game da ko Sin ta samu goyon baya daga kasashen duniya da dama, yayin da mai yiwuwa matsalar cinikayya a tsakanin ta da Amurka ta kara tsananta?.

Hua Chunying ta yi nuni da cewa, Sin da Amurka manyan kasashen duniya ne, kuma sun yi hadin gwiwa sosai a fannin tattalin arziki, don haka ya kamata su girmama juna, da yin zama daidai wa daida da juna, da ci gaba da aiwatar da hadin gwiwa don samun moriyar juna. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China