in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Amurka na gudanar da wata tattaunawar manyan jami'ai domin kokarin karfafa dangantakar tattalin arzikinsu
2016-11-24 10:24:10 cri
Kasashen Sin da Amurka sun tafiyar a ranar Laraba da tattaunawarsu ta shekara shekara ta manyan jami'ai, dake da burin karfafa dangantaka tsakanin manyan tattalin arzikin duniya biyu. Haka kuma tattaunawar nada manufar tabbatar cewa sauyin shugaban kasa a Amurka ya bayyana ta hanyar wani wucin gadi mai armashi a bangaren huldar dangantaka dake tsakanin kasashen biyu.

Abu na farko, ya kamata mu zurfafa daidaita sabane sabane dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, da tabbatar da wani wucin gadi mai armashi domin dangantakar tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Amurka a yayin shigowar sabuwar gwamnatin Amurka, in ji mataimakin faraministan kasar Sin Wang Yang a yayin bude zaman taro karo na 27 na kwamitin hadin gwiwa na Sin da Amurka kan tattalin arziki da musanya (JCCT). Wannan ita ce tattaunawar tattalin arziki ta manyan jami'ai ta karshe tsakanin kasashen biyu a karkashin gwamnatin Barack Obama.

Abu na biyu, bangarorin biyu zasu fafada fannonin dangantakarsu, da samar da karin sakamako na hakika a fannin zuba jari tare, da tattalin arziki da fasahohin zamani da tsaron abinci.

Abu na uku, mataimakin faraministan Sin yayi kira ga bangarorin biyu da su mayar da JCCT wajen samar da karin kayayyaki da moriya, da kuma kara bunkasa matsayinta a cikin dangantakar tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu.

Sakataren kasuwancin Amurka, Penny Pritzker, ya nuna cewa JCCT ya maida kokarinsa kan bangarori mafi dacewa domin dangantaka, lamarin da ya bada dama wajen bunkasa kasuwanci da musanya tsakanin kasashen biyu a tsawon shekaru uku na baya bayan nan. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China