in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yabawa Rwanda game da goyon bayan rundunar hadin gwiwa ta yankin Sahel
2018-03-24 13:14:21 cri
Tarayyar Afrika ta yabawa kasar Rwanda bisa gudunmuwarta ga rundunar kawance ta G5 Sahel, wadda ke da nufin inganta tsaro da yaki da ta'addanci a yankin sahel.

Kasashe 5 da suka hada da Burkina Faso da Chadi da Mali da Mauritania da Niger ne suka kafa rundunar G5 a shekarar 2014, da nufin inganta hadin kai a yankin da kuma magance kalubale na bai daya da suke fuskanta.

A gefen taron AU kan yankin ciniki cikin yanci na nahiyar Afrika ranar Alhamis da ta gabata a birnin Kigali, shugaban Rwanda Paul Kagame ya sanar da bayar da gudunmuwar dala miliyan 1 domin tallafawa ayyukan rundunar.

Cikin wata sanarwa da aka fitar a jiya Juma'a, Paul Kagame ya lashi takobin kasar za ta ci gaba bada goyon baya ga rundunar.

Da yake yabawa kokarin Rwanda ga rundunar, Shugaban hukumar AU Moussa Faki Mahamat, ya ce gudunmuwar ta bayyana irin karfin hadin kai dake tsakanin kasashen dangane da yaki da ta'addanci da sauran laifuka.

Har ila yau, Moussa Faki Mahamat ya roki kasashe mambobin AU su mara baya ga kasashen kungiyar G5. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China