Sakatare janar na MDDr ya mika sakon ta'aziyya ga al'ummar kasar Afrika ta kudu da kuma iyalan marigayiya Madikizela-Mandela.
Ita dai Madikizela-Mandela ta mutu ne a jiya Litinin a Johannesburg, kuma ta rasu tana da shekaru 81 a duniya. Ta rasu ne a daidai lokacin da take karkashin kulawar iyalanta bayan ta shafe tsawon lokaci tana fama da jinya, lamarin da yasa aka yi ta dawainiyar kaita asibiti don nema mata magani tun a farkon wannan shekarar, kamar yadda iyalanta suka tabbatar da hakan.
Madikizela-Mandela ta kasance daya daga cikin jigo wajen fafutukar yaki da wariyar launin fata.(Ahmad Fagam)