in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zaizayar kasa ta hallaka mutane fiye da 100 a Kongo Kinshasa
2017-08-19 12:30:40 cri
Wani jami'in kasar Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, ya shaidawa manema labaru a jiya Jumma'a cewa, bala'in zaizayar kasa da ya abku a arewa maso gabashin kasar a ranar Alhamis da ta gabata, ya haddasa asarar rayukan mutane fiye da dari.

Rahotanni sun ce, tun daga daren ranar Laraba, aka fara mamakon ruwan sama a yankin tabkin Albert dake lardin Ituri na kasar, lamarin da ya haddasa bala'in zaizayar kasa kashegari.

A nashi bangare, Pacifique Keta, mataimakin babban Gwamnan lardin Ituri, ya fadawa manema labarai cewa, zuwa yanzu kasa da laka sun binne a kalla gidajen iyalai 50 a wasu kauyuka 3, sa'an nan yawan mutanen da suka rasa rayukansu ya karu zuwa tsakanin 150 zuwa 200.

A cewar jami'in, gwamnatin kasar ta riga ta tura karin kungiyar aikin ceto zuwa wurin da bala'in ya abku don kai dauki.

Tabkin Albert ya kasance cikin yankin babban tabki dake gabashin Afirka, inda yake kan iyakar dake tsakanin jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo da kasar Uganda. Sannan ya kasance tabki mafi girma na 7 a nahiyar Afirka. Ana samun ruwan sama sosai a wuraren dake dab da tabkin, lamarin da kan haddasa bala'in zaizayar kasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China