A cewar rahoton, bayan shekaru masu yawa da ake ta kokarin raya yankin yammacin Afirka, karuwar tattalin arzikin yankin ya tsaya kan kashi 0.5% kawai a shekarar 2016. Kana manyan dalilan da suka haddasa wannan tsaiko sun hada da raguwar farashin wasu sinadarai, da kuma koma bayan tattalin arzikin kasar Najeriya, bisa la'akari da yadda karfin tattalin arzikin Najeriya ya kai kashi 70% na daukacin yankin.
Ban da haka kuma, wata jami'ar bankin AFDB mai kula da yankin yammacin Afirka ta ce, wani babban kalubalen da ake fuskanta a yankin shi ne na batun samar da guraben aikin yi ga matasa.(Bello Wang)