in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi murna da sako 'yan matan makaranta a Najeriya
2018-03-22 10:23:08 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya bayyana a jiya Laraba cewa, yana matukar farin ciki game da sako mafi yawa daga cikin 'yan mata 110 da aka sace a Najeriya a watan Fabrairu, inda aka kubutar da su lami lafiya.

Ana zargin dakaru 'yan ta'adda na Boko Haram da sace 'yan matan. Cikin jawabin Antonio Guterres da aka gabatar ta bakin kakakinsa, Stephane Dujarric, babban sakataren ya kalubalanci wadanda suka aikata wannan zamba da su saki dukkan 'yan matan da aka sace ba tare da gindaya wani sharadi ba, sa'an nan a ba su damar komawa gidajensu lami lafiya.

Ban da haka kuma, babban sakataren MDD ya bukaci hukumomi daban daban na Najeriya da su yi kokarin gurfanar da wadanda suka saci 'yan matan a gaban kotu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China