Shugaban sashen ayyuka na cibiyar takaita fitar da hayaki mai gurbata muhalli daga ababen hawa na ma'aikatar kare muhalli ta kasar Sin Ma Dong, ya ce nahiyar a yanzu, na da hanyoyi da dama na samun kudi da damarmakin hadin gwiwa wajen samar da ababen hawa marasa gurbata muhalli a birane.
Yayin taro kan amfani da ababen hawa marasa gurbata muhalli da aka kammala jiya a birnin Nairobin kasar Kenya, Ma Dong ya ce Afrika na da damar amfana daga kawancen kasashe masu tasowa dake tsakanin nahiyar da kasar Sin. (Fa'iza Mustapha)