in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci a gudanar da zagaye na 2 na zaben shugaban kasar Sierra Leone lami lafiya
2018-03-16 10:32:18 cri
Tarayyar Afrika AU, ta yabawa babban zaben kasar Sierra Leone da ya gudana ranar 7 ga watan nan, tana mai bayyana shi a matsayin sahihin zaben da aka gudanar cikin kwanciyar hankali.

Yayin da kasar ke tunkarar zagaye na 2 na zaben shugaban kasar cikin makonni 2 masu zuwa, tarayyar, ta yi kira ga masu ruwa da tsaki kan harkokin zabe, musammam 'yan takarar jam'iyyun SLPP da na APC, su tabbatar da dorewar zaman lafiya tare da yin dukkan mai yiwuwa wajen tabbatar da an yi nasarar kammala zaben.

Ya kara da cewa, kudurin AU shi ne mara baya ga karfafa tsarin demokradiyya a Sierra Leone da sauran kasashe mambobinta, ta hanyar gudanar da sahihin zabe mai cike da adalci da kwanciyar hankali. ( Fa'iza Mustapha )

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China