in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha: Za a tsagaita bude wuta a yankin Guta na Gabas na Syria
2018-02-27 10:27:38 cri
Sergey Shoygu, ministan tsaron kasar Rasha, ya fada a jiya Litinin cewa, za a kaddamar da tsagaita bude wuta a yankin Guta na Gabas na kasar Syria don a samu damar kwashe fararen hula wadanda suka jikkata daga yankin.

Shoygu ya bayyana hakan ne a birnin Moscow, fadar mulkin kasar Rashar, inda ya ce, wannan niyya ce da shugaba Vladimir Putin na kasar ya riga ya tsayar da ita. A cewarsa, shirin tsakaita bude wutar ya fara ne daga ranar 27 ga watan da muke ciki, za a gudanar da tsagaita bude wuta tsakanin karfe 9 har zuwa karfe 2 da rana, don ba da damar gudanar da ayyukan jin kai. Ban da haka kuma, za a bude wata hanya ta musamman a yankin Guta na Gabas domin fararen hula su bi wannan hanya su tsira.

Yankin Guta na Gabas ya kasance a karkara dake gabashin birnin Damascus, fadar mulkin kasar Syria. Wasu dakaru masu kin jinin gwamnati sun kwace ikon yankin a shekarar 2012, daga bisani sojojin gwamati sun kewaya wurin har tsawon shekaru 5, amma har zuwa yanzu ba su samu damar shiga cikin yankin ba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China