in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Beijing za ta gina sabbin gidaje tare da yi wa wasu kwaskwarima domin iyalai 23,550
2018-03-05 11:11:47 cri
Beijing na shirin gina sabbin gidaje ko yi wa wadanda suka lalace kwaskwarima domin iyalai 23,550 da ke zaune a gidajen da suka lalace a fadin birnin.

Sanarwar da gwamnatin birnin ta fitar, ta ce za a yi aikin gyara gidaje 236 da suka mamaye kadada 13, 430 a bana. Ta kara da cewa, wasu iyalai 15,300 ko kuma kaso 65 na wadanda za su ci gajiyar gidajen na zaune ne a gundumomi 6 na bayan gari.

Manufar aikin yi wa gidajen kwaskwarima ita ce, daukaka daraja da ingancin rayuwar mazaunan.

Gyaran gidajen da suka lalace na ci gaba da zama muhimmin batu ga gwamnati a shekarun baya-bayan nan. Kididdigar da hukumomi suka yi ta nuna cewa, ko a shekarar da ta gabata, kasar Sin ta sake gina gidaje miliyan 6 ga mazaunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China