in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin zata karbi bakuncin taron mutun-mutumi na duniya
2017-08-09 10:04:44 cri
Kimanin masu basirar kere kere 300 da kuma wakilai daga kamfanonin kera mutun-mutumi 150 ne zasu hallara a birnin Beijing daga ranar 23 zuwa 27 ga watan nan na Augasta, domin halartar gagarumin taron mutun-mutumi na duniya na shekarar 2017 wanda za'a gudanar.

Jami'an ma'aikatar masana'antu da yada labarai ta kasar Sin MIIT, sun tabbatar da cewa, akwai wakilai daga jami'o'i, da cibiyoyin bincike, da kamfanoni da za su halarci taron, inda zasu tattauna game da irin damammakin da ake da su a fannin kera mutun-mutumi.

Kasar Sin ta kasance kasa mafi girma a duniya dake samar da kamfanonin kera mutun-mutumi cikin shekaru 3, lamarin da ya ba ta damar samar da kashi 25 cikin 100 na adadin mutun-mutumi na duniya baki daya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China