in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan tawayen Sudan sun zargi bangaren gwamnati da laifin saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2018-03-05 10:46:02 cri
Gamayyar kungiyar 'yan tawayen Sudan ta (SPLM) tsagin arewacin kasar, ta zargi bangaren gwamnatin kasar da yin fatali da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a jihar Blue Nile.

Kakakin SPLM tsagin arewaci, Mubarak Ardol, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, gwamnatin kasar ta sake saba yarjejeniyar tsagaita bude wutar inda ta afkawa magoya bayan kungiyar 'yan tawayen a jihar Blue Nile.

Ardol ya bayyana cewa, mayakan 'yan tawayen sun dakile wasu hare haren da dakarun gwamnatin Sudan suka kaddamar kansu a safiyar Asabar din da ta gabata inda suka shafe tsawon sa'a guda suna gwabzawa da dakarun gwamnatin a yankin Al-Rum dake jihar ta Blue Nile.

Sai dai kawo yanzu dakarun sojin kasar Sudan din ba su mayar da martani ba game da ikirarin da 'yan tawayen suka yi.

Mayakan SPLM/ tsagin arewaci sun jima suna arangama da dakarun gwamnatin Khartoum a kudancin jihohin Kordofan da Blue Nile tun a shekarar 2011, duk da yarjejeniyar shirin tsagaita bude wutar da aka kulla a lokuta da dama tsakanin bangarorin biyu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China