in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar dake mulkin Sudan ta sauke mataimakin shugaban jam'iyyar
2018-02-22 12:42:46 cri
Jam'iyyar (NCP) mai mulki a kasar Sudan ta sanar da sauke mataimakin shugaban jam'iyyar Ibrahim Mahmoud Hamid inda ta maye gurbinsa da Faisal Hassan Ibrahim.

Ofishin gudanarwar shugabancin jam'iyyar ta NCP ya sanar da daukar wannan mataki ne bayan wata doguwar ganawa da ya yi a ranar Laraba, wanda shugaban kasar kuma shugaban jam'iyyar NCP mai mulki Omar al-Bashir ya jagoranta.

Al Bashir ya fadawa 'yan jaridu cewa, "shugabancin jam'iyyar yana bayyana godiyarsa ga Injiniya Ibrahim Mahmoud Hamid, tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar NCP, kuma an maye gurbinsa da Faisal Hassan Ibrahim".

Wannan dan takaitaccen sauyi da aka samu a tsarin shugabancin jam'iyyar mai mulki ana sa ran zai haifar da yin garambawul a majalisar ministocin kasar a nan gaba, da suka hada da sauye sauyen mukamai a ma'aikatun gwamnatin kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China