Guterresd ya ce kudurin kwamitin sulhun zai yi tasiri ne kadai, idan har aka aiwatar da shi yadda ya kamata. Kamar yadda ya bayyana yayin da yake jawabi a zaman bude taron hukumar kare hakkin bil-Adan ta MDD karo na 37.
A ranar Asabar ne dai kwamitin sulhun MDD ya amince da kudurin ba tare da wata hamayya ba. (Ibrahim)