in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bayyana damuwa game da rikicin kudancin Libya
2018-03-02 09:21:51 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake Libya UNSMIL, ya bayyana damuwa game da rikicin birnin Sabha na kudancin Libya, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula.

Shirin ya ce ya damu matuka da ta'azarar rikicin na Sebha, inda a kalla fararen hula 6 suka mutu yayin da wasu 9 suka jikkata.

Ya kara da cewa ana kai hari kan asibitin birnin akai akai, yana mai cewa dole ne a dakatar da kai hari kan al'umma.

An shafe kwanaki ana kwabza rikicin kibilanci a birnin Sahba dake da nisan kilomita 800 daga kudu maso yammacin birnin Tripoli.

Birnin na fuskantar rashin tsaro saboda karuwar laifufuka da sace sace da kungiyoyi masu dauke da makamai ke yi tare kuma da rikicin kabilanci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China