in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun tsaron kan iyakoki za su murkushe 'yan tada kayar baya a tafkin Chadi
2018-02-28 09:51:38 cri
An bukaci dakarun hadin gwiwa na kasashen duniya (MNJTF) masu yaki da kungiya mai tsattsauran ra'ayi ta Boko Haram a tafkin Chadi da su kara azama tare da yin hadin gwiwa wajen kawar da mayakan 'yan tada kayar bayan domin baiwa al'ummomin fararen hula dake yankunan kariya.

Kwamandan dakarun tsaro, Maj.-Gen. Lucky Irabor, ya fada a Abuja, babban birnin Najeriya cewa, ya zama tilas mambobi kasashe na tafkin Chadi su kara himma wajen yakar 'yan tada kayar bayan wadanda suka kasance makiyan kasashen. Ya bayyana hakan ne a lokacin taron kasa da kasa da aka shirya game da tafkin Chadi, da nufin sanar da duniya kan irin dunbun tattalin arziki dake yankin, da kuma kalubalolin dake addabar tafkin wanda ke fuskantar barazanar kafewar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China