in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: An cimma burin dakile gurbacewar iska
2018-02-27 11:54:30 cri
Ma'aikatar kiyaye muhalli ta kasar Sin ta sanar a yau Talata cewa, bisa matakan da aka dauka a shekaru 5 da suka gabata, yanzu an samu nasarar dakile matsalar gurbacewar iska, tare da inganta yanayin iskar a kasar sosai. Idan aka dubi abubuwan da aka tanada cikin shirin kasar na daidaita matsalar gurbacewar iska, za a ga dukkan burikan da aka sanya a gaba, an samu damar cimma su.

A cewar ma'aikatar, matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka cikin shekaru 5 da suka wuce, sun hada da rufe wasu tsoffin masana'antu masu yin amfani da tsoffin fasahohi, da kara yin amfani da makamashi mai tsabta, da rage kona makamashin kwal, da gyaran fuska a fannonin da suka shafi ayyukan samar da wasu sinadaran da ka iya gurbata muhalli, gami da kyautata tsarin sa ido kan ingancin iska.

Ma'aikatar kiyaye mutalli ta kasar Sin ta kara da cewa, har yanzu ana fama da matsala mai tsanani ta gurbacewar iska a wasu wuraren kasar, da wasu lokuta, don haka ana shirin tsara wata manufar ta shekaru 3 don tabbatar da kara tsabtace iska a kasar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China