in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Rasha: kasashen Rasha da Sin na hadin kai kan batutuwan duniya yadda ya kamata
2018-01-16 09:49:46 cri
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov ya ce, kasarsa da kasar Sin sun dade suna gudanar da hadin kai yadda ya kamata a wasu muhimman batutuwan kasa da kasa da suka shafi zirin Koriya, Syria da sauransu.

Lavrov ya bayyana haka ne a yayin da yake ba da amsa kan tambayoyin 'yan jaridar kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin, a yayin taron manema labaru da aka shirya jiya Litinin game da ayyukan diflomasiyyar Rasha a shekarar 2017, inda ya nuna cewa, kasashen Rasha da Sin sun tsara taswirar warware matsalar zirin Koriya, kana za su ci gaba da goyon bayan gudanar da shawarwari kai tsaye a tsakanin bangarorin da batun ya shafa. Game da batun Syria kuwa, ministan ya ce kasashen Rasha da Sin suna tsayawa tsayin dak na ganin an warware matsalar a siyasance ta hanyar martaba kudurorin MDD da batun ya shafa. A ganinsu, kamata ya yi a shigar da dakarun dake adawa da gwamnatin kasar cikin shawarwarin siyasar, ta yadda za a samu wakilcin kowane bangare. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China