in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a gaggauta daidaita batun Syria
2018-02-23 10:17:49 cri
wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa su taimakawa kasar Syria, don bangarorin dake adawa da juna su samu damar cimma masalaha tsakaninsu bisa tattaunawa, ta yadda za a kyautata yanayin aikin jin kai a kasar.

Wakilin na kasar Sin ya bayyana haka ne a wajen taron kwamitin sulhu na MDD da aka kira a jiya Alhamis don tattauna batun Syria.

Ma Zhaoxu ya ce, kasarsa na tausayawa jama'ar Syria, la'akari da wahalhalun da suka sha sakamakon wutar yaki. Sa'an nan a ganin kasar Sin, neman daidaita yanayin a siyasance ita ce hanya daya tak da bangarori masu ruwa da tsaki za su iya bi. Matakin da ake bukatar dauka a yanzu shi ne, tabbatar da komawa teburin sulhu bisa shiga tsakani da MDD ke yi, da kokarin neman wata manufa da dukkan bangarorin kasar za su amince da ita. Yana mai cewa, ta wannan hanya ne za a samu damar fitar da jama'ar kasar daga mawuyacin halin da suke ciki. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China